Monday, April 28, 2025
spot_imgspot_imgspot_imgspot_img

Katsina state government

HomeLabaraiMajalisar Dokokin Kano Ta Dumama Kan Muƙamin Ganduje

Majalisar Dokokin Kano Ta Dumama Kan Muƙamin Ganduje

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta shiga kika-ƙaƙa a lokacin da Kakakin Majalisar, Jibril Isma’il Falgore, ya kira tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, a matsayin muƙaddashin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa yayin da yake aike wa da saƙon ta’aziyya ga matar Ganduje, Farfesa Hafsat Ganduje, kan rasuwar mahaifiyarta.

Wannan kiran ya haifar da muhawara mai zafi, musamman daga Shugaban Marasa Rinjaye, Labaran Abdul Madari, da wasu ‘yan majalisar APC, waɗanda suka ce Ganduje ya kamata a kira shi da cikakken shugaban jam’iyyar, ba muƙaddashi ba.

Saboda wannan saɓani, zaman majalisar ya kasance an ɗage shi har zuwa ranar Talata.

Wannan zaman ya kasance na farko tun bayan da majalisar ta dawo daga hutun kwanaki 48. Hutun ya biyo bayan zartar da dokar soke masarautu biyar a Jihar Kano, inda jinkirin dawowar ke da nasaba da matsalolin tsaro da suka taso bayan wannan muhimmin sauyin dokar kamar yadda jaridar Nigerian Tracker smta rawaito.

Leadership Hausa

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -
Google search engine

Most Popular

Recent Comments