Monday, April 28, 2025
spot_imgspot_imgspot_imgspot_img

Katsina state government

HomeLabaraiGwamnatin Borno Da UNICEF Sun Hadin Gwiwa Dan Dakatar Da Yin Tsugunno...

Gwamnatin Borno Da UNICEF Sun Hadin Gwiwa Dan Dakatar Da Yin Tsugunno A Fili

Daga Ahmed Liman Kingimi

Gwamna Babagana Zulum, wanda mataimakinsa Umar Kadafur ya wakilta, ya bukaci mazauna yankin da su goyi bayan wannan shiri na tsaftar jihar Borno. Gangamin ya yi daidai da mayar da hankali ga jihar kan muhimman sassa kamar ilimi da lafiya.

Shugabar ofishin UNICEF na Maiduguri, Gerida Birukila, ta yaba da kokarin Borno, inda ta jaddada bukatar daukar matakin hadin gwiwa don kawo sauyin halayya. Mai ba da shawara kan Ilimi na Babbar Hukumar Burtaniya, James Donoghue, ya yaba da ci gaban da aka samu a makarantun firamare, musamman ta hanyar shirin ‘Koyarwa a matakin da ya dace.

Hukumar tana hada kai da masu ruwa da tsaki don dorewar shirin fiye da tallafin da ake samu a yanzu.

Manajan Ilimi na UNICEF Munamuzunga Sikaulu, ya bayyana manufar shirin na inganta sakamakon koyo ga dalibai a matakin farko.

Shugaban ofishin UNICEF na Borno, Phuong Nguyen, ya jaddada mahimmancin tsaftar muhalli don hana al’amuran kiwon lafiya da tallafawa ilimi. An karrama kananan hukumomin Biu da Shani saboda samun matsayin da ba a yi bayan gida a fili ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -
Google search engine

Most Popular

Recent Comments