Sunday, April 27, 2025
spot_imgspot_imgspot_imgspot_img

Katsina state government

HomeLabaraiKungiyar Gwadago Ta Nisanta Kanta Kan Takardar Bogi A Jihar Yobe

Kungiyar Gwadago Ta Nisanta Kanta Kan Takardar Bogi A Jihar Yobe

Daga, Sani Gazas Chinade, Damaturu

Kungiyar Kwadago ta kasa NLC reshen Jihar  Jihar ta bada sanarwar nesanta kanta da  Wata sanarwar da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani, wadda ke  kira ga ma’aikatan jihar Yobe da su shiga yajin aikin gama gari daga ranar 1 ga watan Disamba da cewar wannan labarin karya ne marar tushe.

A wata sanarwa da wakilinmu ya samu yau asabar dauke da sa hannun shugaban kungiyar ta NLC reshen jihar Yobe, Muktar Musa Tarbutu, na cewa kwamitin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da NLC ya kammala tattaunawa kan sabon mafi karancin albashi, kuma an mika rahoton ga gwamna Mai Mala Buni don neman sahalewar sa.

Dom haka kungiyar kwadagon  NLC ta bukaci daukacin ma’aikatan jihar Yobe da su yi watsi da wannan sanarwa ta bogi su ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum.

An kuma gargadi jama’a da su yi taka-tsan-tsan da yada  labaran karya tare da tantance labari kafin a yada shi

Kungiyar NLC ta jihar Yobe za ta ci  gaba da jajircewa wajen ingantawa da kare hakki da muradun ma’aikatan jihar Yobe.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -
Google search engine

Most Popular

Recent Comments