Monday, April 28, 2025
spot_imgspot_imgspot_imgspot_img

Katsina state government

HomeLabaraiAn Sa Dokar Hana Fita Ta Sa’o’i 24 A Kaduna

An Sa Dokar Hana Fita Ta Sa’o’i 24 A Kaduna

Kwamitin tsaro na jihar Kaduna ya sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a cikin garin Kaduna da Zariya. Hukuncin kuma ya fara aiki nan take.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan ya fitar a ranar Litinin.

“Majalisar tsaro ta jihar Kaduna a karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani, bayan ta duba yanayin tsaro a jihar, ta na sanar da ‘yan jihar Kaduna cewa:

“Akwai isassun hujjoji da ke nuna wa karara cewa, zanga-zangar da ake ci gaba da yi, wasu bata-gari sun mamaye ta inda suka fara lalata dukiyoyin jama’a.

“Saboda wannan abin takaici, Majalisar Tsaro ta Jihar Kaduna, ta yanke shawarar kafa dokar hana fita ta sa’o’i 24 a garuruwan Kaduna da Zariya da kewaye, nan take.

”An shawarci mazauna jihar da su kasance a cikin gida yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da kokarin tabbatar da tsaro.” In ji sanarwar

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -
Google search engine

Most Popular

Recent Comments