Monday, April 28, 2025
spot_imgspot_imgspot_imgspot_img

Katsina state government

HomeLabaraiMai Ba Gwamna Buni Shawara Na Musamman Kan Harkokin Tsaro A Yobe...

Mai Ba Gwamna Buni Shawara Na Musamman Kan Harkokin Tsaro A Yobe Ya Gargadi Baban Bola Su Guji Shigowa Jihar Da Tsoffin Karafa

Daga, Sani Saleh Chinade, Damaturu

Ofishin mai ba gwamnan jihar Yobe shawara na musamman kan harkokin tsaro Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam, ya gargadi al’umma musamman masu fasa karafa da aka fi sani da Baban Bola, da su guji shigowa Jihar ta Yobe da tarkace da sauran karafa da aka yi watsi da su daga wasu wurare zuwa cikin jihar.

A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban mai bada shawarar (SA) na cewa, “wannan gargadin ya zama dole ne biyo bayan tarwatsewar wasu bama-bamai da aka  yi watsi da su  da wasu ‘yan ta’addan da  suka tsallako daga cikin dajin Sambisa tun a baya suka ajiye  a yankin Goniri yadda  suka raunata biyar daga cikinsu.”

Don haka ana shawartar jama’a da su kai rahoton duk wani abu da ake tuhuma ko motsin Wasu  mutanen da ba’a yarda da su ba a cikin al’ummominsu.

Sanarwar ta kara da cewar sashen kawar da bama-bamai na soji na aiki ba dare ba rana don kwashe wasu na’urori da watakila an yi watsi da su a shekarun baya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -
Google search engine

Most Popular

Recent Comments