Monday, April 28, 2025
spot_imgspot_imgspot_imgspot_img

Katsina state government

HomeLabaraiƘananan Hukumomi 3 A Kano Ambaliyar Ruwa Ta Shafa — SEMA

Ƙananan Hukumomi 3 A Kano Ambaliyar Ruwa Ta Shafa — SEMA

Hukumar ta gargaɗi mazauna jihar da su guji zubar da shara a magudanan

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Kano (SEMA), ta bayyana cewar ambaliyar ruwa ta lalata wasu yankuna a ƙananan hukumomin Sumaila, Kibiya da Tudun Wada a jihar.

Sakataren hukumar, Alhaji Isyaku Abdullahi Kubarachi ne, ya bayyana haka a yayin taron masu ruwa da tsaki.

Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMET), ta yi gargaɗin cewar akwai ƙananan hukumomi 14 a jihar da ka iya fuskantar ambaliyar ruwa.

SEMA, ta ziyarci yankuna da abin ya shafa don tantance irin ɓarnar da ruwa ya yi tare da miƙa rahoto ga gwamnatin jihar don ba su tallafi.

Hukumar za a tabbatar da adadin mutane ko gidajen da abin ya shafa bayan haɗa rahoton.

Kwanan nan, SEMA da sauran masu ruwa da tsaki sun ziyarci yankunan da ake tsammanin fuskantar ambaliya don wayar musu da kai dangane da hatsarin da ke tattare da madatsar ruwa ta Tiga.

A yayin wannan ziyara, an wayar da kan al’ummar yankunan kan yadda za su shawo kan ambaliya.

SEMA ta bayar da shawar gina madatsar ruwa ta wucin gadi don kare waɗannan yankuna.

Hukumar Kula da Yara ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF), ta bayar da tallafi ta hanyar bai wa mazauna yankunan horo da kuma tallafin kuɗi.

Ko’odinetan Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), Dokta Nura Abdullahi, ya jaddada muhimmancin sarrafa shara yadda ya dace don kaucewa aukuwar ambaliyar ruwa, musamman a birane.

Ya yi kira ga jama’a su daina zubar da shara a magudanan ruwa.

Ya yi kira ga jama’a su daina zubar da shara a magudanan ruwa.

Taron, wanda UNICEF ta tallafa, ya haɗa da wakilai daga ƙungiyoyi daban-daban a jihar.

Aminiya

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -
Google search engine

Most Popular

Recent Comments