Monday, April 28, 2025
spot_imgspot_imgspot_imgspot_img

Katsina state government

HomeLabaraiMutane 14 Sun Rasu Samakon Hatsarin Mota A Jigawa

Mutane 14 Sun Rasu Samakon Hatsarin Mota A Jigawa

Wani hatsarin mota ya lakume rayukan mutane 14 a kan babbar hanyar Kanya a Jihar Jigawa.

Wani hatsarin mota ya lakume rayukan mutane 14 a kan babbar hanyar Kanya a Jihar Jigawa.

Wasu mutane hudu na asibiti a sakamakon hatsarin na ranar Talata tsakanin wata tirela kirar DAF da wata bas kirar Toyota Hiace.

Motocin biyu sun yi karo ne gaba-da-gaba a kusa da wani shingen binciken babban hawa na jami’an hukumar shige da fice.

Ganau sun bayyana cewa Hiace din da ke mugun gudu ce ta yi kokarin wuce wata mota, wanda hakan ya yi sanadin karonta da DAF din.

Jami’an lafiya a asibitin Kanya Babba Cottage sun tabbatar da adadin mamatan da kuma wadanda suka ji rauni a sakamakon hatsarin.

Kakakin ’yan sand ana Jihar Jigawa, DSP Lawan Shiisu Adam, ya ce rundunar ta fara bincike kan lamarin, musamman kan zargin mugun gudun bas din.

Aminiya

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -
Google search engine

Most Popular

Recent Comments