Saturday, April 26, 2025
spot_imgspot_imgspot_imgspot_img

Katsina state government

HomeIlimiGwamnatin Borno Za Ta Dauki  Nauyin Daliban Jihar Zuwa Kasar Sin Don...

Gwamnatin Borno Za Ta Dauki  Nauyin Daliban Jihar Zuwa Kasar Sin Don Yin Karatun Sinanci 

Daga, Muhammad Sani Chinade, Maiduguri

Gwamnatin jihar Borno ta kudurta daukar nauyin daliban Jihar da ke son yin karatun Sinanci a kasar Sin.

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin babban Sakataren Hukumar ba da tallafin karatu ta Jihar Borno, Bala Isa a wata hira da manema labarai a Maiduguri.

Bala ya ce baya ga harshen Sinanci, Gwamna Babagana Zulum ya kuma amince da bayar da tallafin karatu na farko a fannin likitanci, (MBBS) da Injiniya a manyan cibiyoyi a kasar Sin ga daliban Jihar da suka cika sharuddan da ya dace kan takardun su na kammala jarrabawar Afirka ta Yamma (WAEC).

A cewarsa, masu neman karatu akan harshen na Sinanci dole ne su sami sakamako mai kyau a fannin fasaha, yayin da su kuma  masu neman kwarewa akan harkokin aikin likitanci da injiniya dole ne su samu sakamako mai kyau akan harshen Turanci, Lissafi, da Wasu bangarorin kimiyya da suka hada da Biology, Chemistry da Physics.

“A cewarsa ya kamata daliban  su sami mafi karancin kashi 75 na sakamako mai kyau a jarrabawar takardar  shaidar Afirka ta Yamma  (WAEC) akan karatun likitanci (MBBS)da kashi 65 a WAEC akan karatun Injiniya, wadda duk Mai bukata ya yi kokari neman yin hakan kafin ranar 15 ga watan gobe na Augusta ta hanyar shiga adireshin da gwamnatin ta samar na yanar gizo musamman ga daliban da ke tsakanin shekara 18 zuwa 25 na haifuwa.” In ji Bala Isa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -
Google search engine

Most Popular

Recent Comments